Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kotu Ta Dakatar Da Babban Bankin Najeriya Daga Sakin Kason Kudade Ga Gwamnatin Ribas


Gwamnan jihar Rivers a Najeriya, Siminalayi Fubara (Facebook/Fubara)
Gwamnan jihar Rivers a Najeriya, Siminalayi Fubara (Facebook/Fubara)

Mai Shari’a Joyce Abdulmalik ta babbar kotun tarayya dake Abuja ta dakatar da Babban Bankin Najeriya daga cigaba da sakin kason kudaden wata-wata ga gwamnatin jihar Ribas.

Mai Shari’a Joyce Abdulmalik tace ci gaba da karba da rarraba kason wata-watan da gwamnan jihar Ribas, Siminalayi Fubara, ke yi ya sabawa kundin tsarin mulki kuma bai kamata a bari ta ci gaba ba.

Alkalin ta cigaba da cewar gabatar da kasafin kudin 2024 da Gwamna Fubara ya yi a gaban majalisa mai wakilai 4 sabawa tanade-tanaden kundin tsarin mulki ne.

Mai Shari’a Joyce Abdulmalik ta kara da cewa abinda gwamnan ya aikata ya yi mummunan cin karo da kundin tsarin mulkin 1999.

A karshe dai alkalin ta dakatar da babban bankin najeriya da babban akanta na tarayya da bankunan Zenith da Access daga cigaba da barin Fubara ya taba kudaden dake cikin asusun tarayya dana tara kudaden shigar gwamnati.

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 3:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 2:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG