Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Hukumar Kare Hakkin Bil Adama Tana Binciken Wuraren da Ake Tsare Mutane


Kungiyoyin kare hakkin bil Adama su na zargin cewa ana mummunan keta hakki a wuraren da ake tsare 'yan Boko Haram da wasu mutanen da aka kama.

Hukumar Kare Hakkin Bil Adama ta Kasa ta Najeriya ta kafa wani kwamitin da zai binciki wuraren da ake tsare mutane cikinsu a fadin Najeriya, a bayan da aka yi ta samun rahotannin kamawa da tsare mutane haka siddan a wuraren da tun farko ba na tsare mutane ba ne.

An damkawa kwamitin binciken karkashin jagorancin Ibrahim Nikau, alhakin “karba, bincike da nazarin duk wani bayani, ko kuka, ko kara ko zargi dangane da wuraren da ake tsare mutane cikinsu haka siddan a duk fadin Najeriya.”

Kungiyoyin kare hakkin bil Adama a fadin duniya, cikinsu har da “Human Rights Watch” da “Amnesty International” sun bayyana damuwa a kan yadda ake keta hakkin jama'a a wuraren da ake tsare mutane, musamman ma a wuraren da ake tsare wadanda ake zargin 'yan Boko Haram ne.

Kwanakin baya ne shugaban Najeriya, Goodluck Jonathan, ya bayarda sanarwar sakin kudi fiye da Naira Biliyan daya domin yin kwaskwarima a barikin Giwa dake Maiduguri da wasu wuraren da sojoji suke yin amfani da su wajen tsare mutanen da suke zaton 'yan Boko Haram ne.

Rundunar sojojin Najeriya dai ta furta cewa da gaske ne tana tsare da daruruwan mutanen da ake zaton 'yan Boko Haram ne ba tare da an gurfanar da su a gaban shari'a ba.

Haka kuma an ba wannan kwamiti na hukumar kare hakkin bil Adama ikon kai ziyara, da dubawa ko nazarin duk wuraren da ake tsare mutane cikinsu a duk fadin Najeriya, ko da wanene yake gudanar da su.
Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG