Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Fashewar Gurneti Ya hallaka Mutum Daya A Ethiopia


Taron gangamin siyasa a Ethiopia
Taron gangamin siyasa a Ethiopia

Mutum daya ya mutu da dama kuma suka ji raunuka yau asabar a wata fashewa da ta auku wajen wani gangamin siyasa a Addis Ababa babban birnin kasar, bisa ga cewar jami’ai.

Sabon Firai Ministan kasar Habasha mai hankoron sauyi, Abiy Ahmed ya kammata jawabi a wurin gangamin ke nan lokacin da gurneti ya tarwatse.

Tashar talabijin ta kasar nan da nan ta dauke daga kan Abiy yayinda aka gaggauta fitar dashi daga dakalin da ya yi jawabin a dandalin Meskel inda dubban mutane suka yi dafifi domin jin jawabin matashin dan siyasar da ya sanya malafa da kuma ‘yar karamar taguwar T-Shirt.

Bayan fashewar Abiy ya fada a wani jawabi da ya yi a gidan talabijin cewa, “kauna tana nasara a ko da yaushe. Kisan wadansu gazawa ne. Ga wadanda ke kokarin raba kawunanmu, ina so in shaida maku cewa ba suyi nasara ba”.

Tunda Firai Minista Abiy ya kama aiki a watan Aprilu ya yi manya manyan canje canje a kasar, da suka hada da sakin dukan ‘yan jarida da aka tsare, da soke laifukan da ake tuhumar ‘yan gwaggwarmaya dake sukar gwamnati, ya kuma dauki matakan bunkasa tattalin arzikin kasar

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG