Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

CNN Ta Hana Kungiyar ‘Yan Jaridar Fadar White House Shiga Zauren Muhawara


Yan takarar neman shugabancin Amurka.
Yan takarar neman shugabancin Amurka.

Kungiyar masu aiko da rahotanni ta Fadar White House ta fada a ranar Alhamis cewa gidan talabijin na CNN ya yi watsi da bukatar baiwa wakilanta damar shiga zauren muhawarar farko ta shugaban kasa tsakanin shugaba mai ci Joe Biden da abokin hamayyarsa Donald Trump na jam’iyyar Republican.

Tawagar ‘yan jaridar, wadda ta kunshi wakilan manyan kungiyoyin labarai, dake tare da shugaban kasa a lokacin balaguron kasashen waje da na cikin gida, kuma a kullum yana samun damar zuwa duk wani taro da zai yi magana ko ya bayyana a bainar jama'a, da nufin sanar da jama'ar Amurka.

Yana da wuya a hana tawagar shiga wani taron a Amurka.

“WHCA ta damu matuka cewa CNN ta yi watsi da bukatar da muka yi ta maimaitawa na hada da wakilin tawagar ‘yan jarida na fadar White House a cikin zauren muhawarar,” in ji Kelly O'Donnell, shugaban kungiyar masu ba da rahoto ta Fadar White House a cikin wata sanarwa.

Wadannan 'yan jarida suna nan don ganin abin da ake fada da aikatawa lokacin da abin magana da kyamarori ke kashe, kuma suna ba da kulawa mai zaman kanta.

O'Donnell ya ce duka kwamitin yakin neman zaben Biden da Trump sun amince da bukatar WHCA.

CNN ta amince da ba da izini ga dan jaridar Fadar White House daya ya shiga zauren muhawarar yayin da aka tafi hutun tallace-tallace.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG