Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

CBN Ya Amince Da Sakin Kunshin Dokokin Musayar Kudade


Babban bankin Najeriya CBN
Babban bankin Najeriya CBN

A cewar sanarwar da CBN din ya fitar, kunshin dokokkin zai zamo jagora ga bangaren bankuna wajen dabbaka halaye nagari a tsakanin dillalan da aka sahalewa yin hada-hada a kasuwar musayar kudaden Najeriya.

Babban bankin najeriya (CBN) ya bayyana cewar ya amince da sakin dokokin musayar kudade na Najeriya.

CBN ya kuma sanarda cewar za’a kaddamar da kunshin dokokin a mako mai zuwa a Abuja.

A cewar sanarwar da CBN din ya fitar, kunshin dokokkin zai zamo jagora ga bangaren bankuna wajen dabbaka halaye nagari a tsakanin dillalan da aka sahalewa yin hada-hada a kasuwar musayar kudaden Najeriya.

Sanarwar ta kara da cewar, “CBN ya amince a saki kunshin dokokin domin yin jagora ga bangaren bankuna wajen dabbaka halaye nagari a tsakanin dillalan da aka sahalewa yin hada-hada a kasuwar musayar kudaden najeriya.

“Babban bankin zai kaddamar da kunshin dokokin a hukumance a babban dakin taro na shelkwatarsa dake abuja, a ranar talata, 28 ga watan Janairun 2025.

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 3:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 2:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG