Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ba Gudu Ba Ja Da Baya A Yajin Aikin Da Muka Fara - Likitocin Najeriya


Kungiyar Likitocin Najeriya
Kungiyar Likitocin Najeriya

Kungiyar likitocin Najeriya ta sha alwashin ci gaba da yajin aikin har sai baba ta gani, duk kuwa da yarjejeniyar da suka rattabawa hannu da gwamnatin tarayya na janye wa'adin shiga yajin aikin.

A jiya Alhamis ne kungiyar likitocin ta shiga yajin aikin na gama-gari a kasar, saboda “kasawar da gwamnati ta yi na biyan bukatunsu, ciki har da biyan albashi da likitocin ke bin gwamnati bashi.

Yajin aikin ya zo ne kwana daya bayan da gwamnati ta yi yunkurin hana likitocin shiga yajin aiki, ta hanyar tattaunawa da su da kuma rattaba hannu akan wata yarjejeniya ta janye shirin shiga yajin aikin a ranar Larabar da ta gabata.

Karin bayani akan: Coronavirus, COVID-19, Chris Ngige, Shugaba Muhammadu Buhari,, Nigeria, da Najeriya.

To sai dai kungiyar ta ce an tilasta mata sa hannu a yarjejeniyar ne ba bisa son ran ta ba a lokacin taron na bangaren gwamnati da shugabannin kungiyar, wanda aka gudanar a ofishin Ministan kwadago Chris Ngige.

Ministan Kwadagon Najeriya Chirs Ngige
Ministan Kwadagon Najeriya Chirs Ngige

Kungiyar likitocin a shafinta na twitter, ta baiwa ‘yan Najeriya hakuri, tare da neman su fahimci yanayin da suke ciki, tana mai bayyana cewa ba ta shiga yajin aikin ne domin kuntatawa ‘yan kasar ba, sai dai domin matsawa gwamnati lambar kara azama wajen sauke nauyin da ya rataya a wuyanta na kula da lafiyar jama’a.

https://twitter.com/nard_nigeria/status/1377523163186278400?s=20

Da yake tabbatar da soma yajin aikin, shugaban kungiyar likitocin Dr. Uyilawa Okhuaihesuyi, ya ce sun gaji da sa hannu akan yarjejeniyoyi da gwamnatin tarayya amma ba’a aiwatarwa, inda ya ce har kawo yanzu ba’a taba aiwatar da wata yarjejeniya ko daya da suka kulla da gwamnati a cikin shekaru 10 da suka gabata ba.

Dr. Uyilawa Okhuaihesuyi, Shugaban Kungiyar Likitocin Najeriya
Dr. Uyilawa Okhuaihesuyi, Shugaban Kungiyar Likitocin Najeriya

Ko baya ga neman biyan albashin da likitoci ke bin gwamnati bashi, kungiyar na kuma bukatar gwamnati da ta kara yawan kudin alawus na hatsarin ma’aikatan kiwon lafiya da sauran hakkokin barazanar yaki da cutar COVID-19 da suke fuskanta a asibitoci.

Haka kuma suna neman a rage yawan kudaden da membobinsu ke biya na samun horo na waje a dukkan manyan manyan makarantun kasar ba tare da wani jinkiri ba.

Yajin aikin na zuwa ne a daidai lokacin da shugaban Shugaba Muhammadu Buhari ya yi balaguro zuwa birnin London domin duba lafiyarsa.

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 3:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 2:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG