Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ana kokarin hana lauyoyin Al-Mustapha daukaka kara?


Major Hamza Al-Mustapha (file photo)
Major Hamza Al-Mustapha (file photo)

Makoni uku bayan da aka yankewa, Major Hamza Al-Mustapha hukuncin kisa,, lauyoyinsa suke kokarin samun hukuncin a rubuce domin su daukaka kara amma ina

An shiga sati na uku ke nan, da wata kotu a birnin Ikko ta yankewa Major Hamza Al-Mustapha hukuncin kisa.

To amma kuma tun daga lokacin kawo yanzu, lauyoyin Al-Mustapha suna safa da marwa domin neman samun wannan hukunci ko shari'a a rubuce, wanda zasu yi amfani dashi wajen daukaka kara.

Wannan al'amari yasa yan uwan Al Mustapha ke cewa kila jita jitan da suke ji cewa za'a sawa Al Mustapha guba a cikin abinci ya zame gaskiya.

A wata hira da sashen Hausa, kanin Al-Mustapha, Hadi Al-Mustapha ya shedawa wakilin sashen Hausa Ladan Ibrahim Ayawa cewa suna jin jita jitan cewa za'a yi kokarin asawa Al-Mustapha guba a cikin abinci domin a tabbata cewa ya mutu.

Hadi yace su dai gwamnati ba zasu saki Al-Mustapha da rai ba, zassu yi iyakacin kokarin su tabbata sun kashe shi.. Amma kuma yace sun bar komai hannun Allah, domin kuwa shekaru goma sha hudu ke nan ake yi musu rashin adalci.

Da wakilin sashen Hausa ya tuntunbi lauyan Al-Mustapha, sai ya ce dashi ya zuwa ranar ashirin da uku ga wannan wata na fabrairu da nake magana da kai, ba'a basu hukuncin a rubuce ba. Yace an gaya musu cewa har yanzu ba'a gama bugawa akan keken rubuta ba.

Lauyan Al-Mustapha yana bukatar wannan hukunci a rubuce domin ya daukaka kara. Ya kuma ce zai ci gaba da neman an bashi wannan hukunci a rubuce, domin ya daukaka kara.

Aika Sharhinka

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG