Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Kammala Taron Makiyayan Afirka A Nijar Kan Makomar Sana’ar Kiwo


Taron makiyaya daga kasashen Afirka da aka gudanar a Nijar
Taron makiyaya daga kasashen Afirka da aka gudanar a Nijar

An kammala wani taron kasa da kasa a Jamhuriyar Nijar na kungiyoyin makiyayan Afirka kan yadda matsalolin tsaro ke yin illa ga sana'ar kiwo da rayuwar makiyaya.

AGADEZ, NIGER - Taron da aka shafe kwanaki uku ana gudanar da shi ya samu halartar kungiyoyin makiyaya daga kasashe na yankin Sahel irinsu Chadi, Mali da kuma Burkina Faso.

Taron Makiyaya a Nijar daga kasashen Sahel
Taron Makiyaya a Nijar daga kasashen Sahel

Makasudin taron shine bitar halin da matsalolin tsaro suka jefa rayuwar makiyaya da yin barazana ga makomar sana’ar kiwo a wadannan kasashe na sahel.

Hamidou Sawadogo, daya daga cikin shugabannin makiyaya na Burkina Faso ya bukaci taimakon gwamnatocin kasashen yankin wajen shawo kan matsalolin tsaron dake rutsawa da su wajen gudanar da harakokinsu

Taron makiyaya a NIjar na kasashen Sahel
Taron makiyaya a NIjar na kasashen Sahel

Ra’ayi dai yana zuwa guda tsakanin shugabannin makiyayan game da kare batun kiwo a wadannan kasashen a cewar Malan Balma, wani makiyayi daga kasar Mali, ya ce akwai bukatar makiyaya su fahimta tare da kiyaye dokokin kasashen yankin wanda hakan zai basu damar gudanar da kiwon nasu ba tare da wata matsala ba saboda wadannan matsalolin na barazana ga makomar kiwo a kasashen.

Mahalarta taron dai sun fito da shawarwari na hanyoyin samar da mafita domin shawo kan wannan matsalar da ta taso ga sanar’ar kiwo.

Saurari cikakken rahoto daga Hamid Mahmud:

An Kammala Taron Makiyayan Afirka A Nijar Kan Makomar Sana’ar Kiwo.mp3
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:39 0:00

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG