Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Likitocin Dabbobi Da Makiyaya A Afrika Ta Yamma Na Taron Bitar Ayyukan Riga Kafi


RIGAKAFIN DABBOBI
RIGAKAFIN DABBOBI

A jamhuriyar Nijar Shugabannin kungiyoyin makiyaya da kwararrun likitocin dabbobi daga kasashen Afrika Ta Yamma na gudanar da taron bita domin tantance tasirin yekuwar riga kafin da aka gudanar akan iyakokin kasashen ECOWAS da nufin murkushe wasu muggan cututtikan da ke hallaka bisashe.

Lura da yadda kai da kawon makiyaya daga wannan kasa zuwa waccan ke zama wata hanyar yada cututtukan dabobi a tsakanin kasashe ya sa kungiyar CEDEAO bullo da yekuwar allurar riga kafin bisashe akan iyakokin kasashe mambobinta dalili kenan bayan kammala zagayen kamfen da aka gudanar a baya bayan nan a daukacin yankin Afrika ta yamma likitocin dabbobi da wakilan kungiyoyin makiyaya su ka hadu a birnin Yamai don bitar wadannan ayyuka.

Makiyayan kasar Ghana na daga cikin wadanda ke dandana kudar cututtukan da ake hangen dakile yaduwarsu a yankin CEDEAO, wakilinsu a wannan taro Imam Hannafi Sunday ya fayyace girmar wannan matsala a kasarsa.

Tasirin riga kafin da aka shirya a baya ya haifar da walwala a wajen makiyayan da abin ya shafa saboda haka su ke ganin bukatar dorewar wannan tsari na kungiyar ECOWAS.

A cewar Souleymane Djibril wani mai halartar wannan zama daga Togo idan so samu ne zai yi kyau a fadada irin wannan tsari zuwa sauran sassan Afrika.

Taron yaki da annobar cututtukkan dabbobi da ya gudana a shekarar 2022 a birnin Abidjan ne ya bullo da tsarin kiran irin wannan haduwa ta bitar yekuwar allurar riga kafi lokaci zuwa lokaci domin kara inganta wannan tafiya ta bai daya a tsakanin kasashen CEDEAO.

A wannan karon bayan shafe kwanaki 4 na musanyar bayanai, tawagogin na likitocin dabobi da shugabannin kungiyoyin makiyaya za su bullo da sabbin shawarwarin da za a gabatar da su ga gwamnatocin kasashen Afrika ta Yamma.

Saurari rahoton:

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:34 0:00

XS
SM
MD
LG