Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Amurka Ta Kakabawa Venezuela Takunkumi Bisa Zargin Yin Magudi a Zaben Kasar


Shugaban Venezuela Nicolas Maduro wanda ya yi tazarce da Amurka ta zargeshi da yin magudi a zaben kasarsa
Shugaban Venezuela Nicolas Maduro wanda ya yi tazarce da Amurka ta zargeshi da yin magudi a zaben kasarsa

Bayan da shugaban Venezuela Nicolas Maduro ya ce ya lashe zaben kasar da 'yan adawa suka gujewa, Amurka ta kakabawa kasar takunkumin da ya hana cinikayya tsakanin kasashen musamman sayan man fetur din ita Venezuelan

Amurka ta saka takunkumin tattalin arziki akan Venezuela a jiya Litinin, saboda abinda ta kira “magudin zabe da aka tafka” a wajen sake zaben shugaba Nicolas Maduro a wa’adin na biyu na tsawon wasu shekaru shida.

Shugaba Trump ya sanya hannu akan wata doka ta shugaban kasa-da zai iya dauka wani umurni na kashin kansa ba tareda izinin majalisa ba, wanda ya haramtawa Amurkawa yin cinikayyar man fetur da kasar ta Venezuela, wacce a da, tana daya daga cikin kasashen duniya da ke gaba-gaba wajen samar da man na fetur.

Hukumomin a Caracas, babban birnin kasar ta Venezuela sun soki labarin takunkumin, inda ministan harkokin kasashen waje, Jorge Arreaza, ya fadawa manema labarai cewa, matakin na Amurka haramatacce ne, yana mai kwatanta shi a matsayin “hauka, gidadanci da kuma keta dokokin kasa da kasa.”

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG