Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Amurka Ta Hakura Da Neman Sojoji Uku Da Suka Bace


Rundunar Sojan Amurka ta dakatar da aikin nemo sojojin kundunbala uku da suka bace bayan da jirginsu yayi hatsari cikin teku.

Rundunar sojan Amurka tace ta hakura, zata watsar da kokarin da take na neman sojojin Amurka guda uku da suka salwance bayan da jirgin samansu ya fadi a cikin teku a kasar Australia jiya Asabar.

An dai ci sa’ar tsamo sauran sojojin kundumbala 23 dake cikin wannan jirgin samfurin MV-22 Osprey da ya abka cikin tekun.

Sanarwar da rundunar sojan kundumabalar suka bada tace yanzu ba neman wadancan sojan ukku suke ba, suna neman gawwawakinsu ne kuma tuni ma an riga an sanarda iyalansu abin da ya faru.

Sanarwar tace daga wani makeken jirgin ruwa mai jigilar jiragen sama ne aka aika jirgin da ya fadi ne zuwa aiyukkan shawagin da aka saba alokacin da wannan hatsarin ya auku.

Shima shugaban Amurka Donald Trump da yanzu ya soma hutu a garin Bedminster na jihar NJ, an sanar da shi game da faduwar wannan jirgin.

Facebook Forum

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 2:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG