Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Al’ummar Nijar Na Kokawa Kan Yadda Kanfanin China Ya Gaza Cika Alkawari


Masu hakar ma'adinai
Masu hakar ma'adinai

Hukumomi da kungiyoyin matasa da tsofaffin ma’aikata sun soki lamirin kanfanin kasar China da ke shirin fara aikin hako ma'adanin uranium a arewacin Nijar da kasa samar da wani ci gaban a zo a gani ga al’ummar da ke rayuwa a yankin tsawon shekarun da ya shafe yana gudanar da aiki.

Wannan na zuwa ne mako guda bayan cimma yarjejeniya da kanfanin ya yi tsakaninsa da mahukunta Nijar

Duk da kasancewar kanfanin na kasar China a matsayin mai alfanu ga yankin arewacin Nijar al’umma da mahukuntan yankin sun ce ba su ga wani abin a zo a gani da kanpanin yayi lokacin da yayi aikin hako karfen uranium a Azelik da ke yankin Ingall a arewacin Nijar.

Masu fafutuka da kare hakkokin bil’adama irinsu almustafa Alhassan sun bayyana cewa tsawon lokacin da kanfanin ya shafe yana aiki a yankin sun yi ma yankin illa matuka ga kuma gurbata muhalli.

A shekara ta 2014 ne kanfanin na China ya rufe kofofinsa a cikin wani yanayi na sa-in-sa tsakaninsa da ma’aikatansa to sai dai gamayyar kungiyoyin matasa na jihar Agadas sun fitar da sanarwa ta neman kanpanin ya sake salon yadda yake ayyukan hako karfen uranim a yankin.

Kanfanin na kasar China zai gina katafariyar tashar samar da wutar lantarkin mai aiki da hasken rana a yankin, wadda tana daga cikin abubuwan more rayuwa da al’ummar yankin za su anfana da ita.

Saurari rahoton Hamid Mahmud:

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:38 0:00

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG