Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Akalla Mutane 40 Suka Mutu Sakamakon Fashewar Tankar Mai A Laberiya


Tankar Mai
Tankar Mai

Akalla mutane 40 ne suka mutu sakamakon fashewar wata tankar iskar gas a Arewa ta tsakiyar kasar Laberiya, a cewar babban jami'in kula da lafiya na kasar ta yammacin Afirka, Francis Kateh, a ranar Laraba.

WASHINGTON, D. C. - Tankar man ta yi hatsari ne da yammacin ranar Talata a Totota da ke karamar hukumar Lower Bong, kuma jim kadan bayan nan ta fashe, lamarin da ya yi sanadiyyar rasa rayuka da jikkata wasu da dama wadanda suka yi tururuwa zuwa wurin.

Mutane da dama ne ke kwance a asibiti sakamakon konewa, kuma adadin wadanda suka mutu na iya karuwa, kamar yadda Kateh ya shaida wa manema labarai.

Rashin kyawun hanyoyin mota da raunin ababen more rayuwa sun sanya yankin na kudu da hamadar Sahara ya zama yankin da ya fi muni a duniya wajen hadurra, inda adadin wadanda ke mutuwa ya ninka na Turai sau uku, a cewar alkaluman Majalisar Dinkin Duniya.

-Reuters

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 3:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 2:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG