Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

AFCON: CAF Ta Soke Karawar Najeriya Da Libya


CAF
CAF

CAF ta wallafa sabon jadawalin gasar a shafinta na X a yau Talata, sai dai, bai hada dana karawar Najeriya da kasar Libya ba.

Hukumar shirya wasan kwallon kafa ta nahiyar Afrika (CAF) ta soke karawar zagaye na 2 na neman gurbin shiga gasar cin kofin Afrika (AFCON) a rukunin “d” tsakanin tawagar “Super Eagles” ta Najeriya da takwararta ta kasar Libya “Mediterranean Knight”.

CAF ta wallafa sabon jadawalin gasar a shafinta na X a yau Talata, sai dai, bai hada dana karawar Najeriya da kasar Libya ba.

Tunda fari an tsara cewar karawar zata gudana a kasar Libya da misalin karfe 8 na yammacin yau Talata bayan da zagayen farko ya gudana a filin wasa na Godswill Akpabio, dake birnin Uyo a Juma’ar data gabata.

Tawagar Super Eagles ta lallasa Mediterranean Knight da ci daya mai ban haushi a daf da tashi daga karawar.

Sai dai, takaddama ta dabaibaye zagaye na 2 bayan da ‘yan wasan Super Eagles da masu kula da kungiyar suka bada labarin taskun da suka shiga na tsawon sa’o’i 14 a filin saukar jiragen saman Libya abin da ya tilasta musu dawowa gida.

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 3:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 2:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG