Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

A Nijar wasu kungiyoyi na shirin yin zanga zangar kin mulkin maka karya


Kasar Nijar
Kasar Nijar

Wasu kungiyoyin rajin kare mulkin dimokradiya a kasar Nijar sun ce sun gano shirin shimfida mulkin kama karya da gwamnatin kasar keyi saboda haka zasu gudanar da zanga zanga cikin 'yan kwanaki masu zuwa

Kungiyoyin sun bayyana cewa wani taron nazari da suka yi akan yadda alamuran mulki ke gudana a kasarsu ta Nijar sun gano alamomi masu karfi na kokarin da gwamnatin kasar keyi domin shimfida mulkin kama karya da talakawanta suka rungumi dimokradiya yau fiye da shekaru ishirin da biyar.

Saboda haka kungiyoyin sun kuduri yakar wannan sabon salon mulkin kasar da Shugaba Muhammad Issoufou yake shimfidawa.

Shugaban kungiyar Muliyan Sirajo Isa yana cikin masu jagorar yunkurin. Yace ba zargi suke yi ba abu ne na gaskiya, kuma tabbatacce a kasar. Misali, yace ba'a yi zabe ba. Wanda aka yi ba'a yishi kan tafarkin dimokradiya. An yi zaben ne bayan da aka yi watsi da kundun tsarin mulki da dokokin zaben kasar. An yi aiki da son kai tare da son rai saboda a biyawa mutum daya bukata, shugaban kasa na yanzu Muhammad Issoufou.

Amma shugaban kawancen kungiyoyin Rosel Abdu Mamman Lokoko mai goyon bayan gwamnatin Issoufou Muhammad na kallon korafin kungiyoyin rajin kare dimokradiya a matsayin mara tushe. Yace kashi sittin cikin dari sun zabi shugaban kasa na yanzu lamarin da ya bashi damar nada firayim minista kana shi kuma ya nada gwamnati.Yace duk wani dan kasa da ya tashi yace bai yadda da shirin ba to da doka yake fada. Idan su 'yan dimokradiya ne na kwarai ya kamata su duba abun da shugaban kasa keyi daidai wanda basu kuma kan ka'ida su kaiwa hukumomin dake kula da irinsu.

Kungiyoyin rajin kare mulkin dimokradiya din dai sun shirya yin zanga zanga ranar ishirin da hudu na wannan watan domin nuna rashin amincewa da salon tafiyar gwamnatin kasar..

Ga karin bayani.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:33 0:00
Shiga Kai Tsaye

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG