Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Gwamnatin Najeriya Ta Bayyana Shirin Kera Jiragen Sama


ABUJA: An sake bude filin jirgin sama na kasa da kasa dake Abuja
ABUJA: An sake bude filin jirgin sama na kasa da kasa dake Abuja

Matakin ya dace da aniyar gwamnatin ta tallafawa kamfanonin jiragen saman Najeriya tare da bunkasa bangaren sufurin jiragen saman.

Ministan sufurin jiragen sama da bunkasa harkokin sararin samaniya, Festus Keyamo, ya bayyana shirin gwamnatin tarayyar Najeriya na kafa kamfanin kera jiragen sama a cikin kasar.

Keyamo ya sanar da hakan ne yayin kaddamar da cibiyar gyare-gyare da yiwa jiragen sama garanbawul tare da tallafawa harkokin sufurinsu a Abuja.

Ya kara da cewa matakin ya dace da aniyar gwamnatin ta tallafawa kamfanonin jiragen saman Najeriya tare da bunkasa bangaren sufurin jiragen saman.

Da yake jaddada muhimmancin aikin, Ministan ya bayyana cewa shigar da karin gine-gine irinsu cibiyar bada horo, wata babbar nasara ce.

Dandalin Mu Tattauna

Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG