Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Aiyedatiwa Ya Lashe Zaben Gwamnan Jihar Ondo


Lucky Aiyedatiwa
Lucky Aiyedatiwa

Hukumar zaben Najeriya ta ayyana Lucky Aiyedatiwa na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar Ondo.

Bayan watanni ana yakin neman zabe, al’ummar jihar Ondo sun kamala zabe a ranar Asabar 16 ga watan Nuwamba, inda Lucky Aiyedatiwa ya lashe zaben da kuri’u mafiya rinjaye.

Aiyedatiwa, gwamnan jihar mai ci ya samu kuri’u 366,781 inda ya doke abokin karawarsa na Jam’iyyar PDP kuma tsohon mataimakin gwamnan jihar Ajayi Agboola, wanda ya samu kuri’u 117,845.

Sanarwar ta zo ne sa'o'i bayan da aka fara tattara sakamakon zaben da sanyin safiyar ranar Lahadi.

Sakamakon karshe ya nuna cewa jam’iyyar APC ta lashe zaben da kuri’u mafiya rinjaye, inda ta yi nasara a duka kananan hukumomin jihar 18.

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 3:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG