Za a fitar da ragowar bayanan kisan shugaba John F. Kennedy

Tsohon shugaban Amurka J. F. Kennedy da maidakinsa Jacie

Yau ake kyautata zaton za a fitar da rukunin karshe na bayanan da suka shafi kisan gillar shugaban kasar Amurka John F. Kennedy,JFK, da mai yiwuwa ya kara haske kan lamarin da ya tada hankalin al’umma da kwararru kan kisan tsohon shugaban kasar.

An kashe shugaba Kennedy ne lokacin da yake tafiya titinan birnin Dallas, jihar Texas cikin mota tare da matarsa Jackie rana 22 ga watan Nuwamba shekara ta dubu da dari tara da casa’in da uku.

Shugaba Donald Trump ya sanar a sakon twitter cewa, zai bada izinin fitar da bayanan karshe na kisan shugaba JFK.

Wani kwararre Larry Sabato, yace Mai yiwuwa fitar da dukan bayanan ya taimaka wajen samun haske kan kisan Kennedy inji