YANAYI DA MUHALLI: Shirin rage radadin matsalar ambaliyar ruwa da aka fuskanta a Najeriya - Nuwamba 04, 2022

Aisha mu'azu

An fuskanci matsalar ambaliyar ruwa a sassan Najeriya da dama, lamarin da ya kai ga asarar rayuka da dukiyoyi.

Yayin da ake ci gaba da agazawa wadanda ambaliyar ruwa ta shafe su a Najeriya, masana harkar sauyin yanayi sun nuna bukatar masu ruwa da tsaki su fara shirin wayar da kan al'umma da kuma daukan mataken karıya domin rage radadin matsalar ambaliyar ruwa da ake fuskanta kusan kowace shelkara a Najeriya.

A latsa nan domin sauraron sautin:

Your browser doesn’t support HTML5

YANAYI DA MUHALLI: Shirin rage radadin matsalar ambaliyar ruwa da aka fuskanta a Najeriya - 7'35"