'Yan bindiga Sun Kashe 'Yan sanda Biyu a Nijar

wata tawagar dakarun Jamhuriyar Nijar

Tun a farkon watan nan, gwamnatin Nijar ta sanar cewa akwai yiyuwar ‘yan ta’adda za su kwatanta kai hari a birnin Yamai mafarin abin da ya sa jami’an tsaro suka kaddamar da wani binciken ababen hawa.

Wasu ‘yan bindiga sun hallaka ‘yan sanda biyu yayin da wasu daban biyu suka ji munanan raunuka bayan da suka kai hari a tashar bincike ta kauyen Goudel Gorou Bongo Banda da ke gab da mashigar birnin Yamai kan hanyar Ouallam.

Wannan na faruwa ne a wani lokacin da ake shirye-shiryen taron shuwagabanin kasashen Afirka da kasar ta Nijar za ta karbi bakuncinsa a farkon watan gobe.

Wakilin Muryar Amurka a Yamai Souley Moumouni Barma ya ruwaito cewa maharan wadanda ba a bayyana yawansu ba sun yi nasarar isa tashar bincike ta kauyen Goudel Gorou ne a kafa da misalin karfe 11 na dare lamarin da ya ba su damar shammatar jami’an tsaro suka bude masu wuta.

Masu nazari akan al’amuran tsaro na kallon wannan hari a matsayin wani abin da aka kitsa da gamin bakin wasu mutanen gari.

Tuni aka jibge karin jami’an tsaro a wannan tashar bincike da kewayenta yayin da ‘yan sanda suka killace wurin da abin ya faru a wani yunkurin harhada bayanan farko na binciken da zai ba da damar tantance zahirin abin da ya wakana.

Tun a farkon watan nan, gwamnatin Nijar ta sanar cewa akwai yiyuwar ‘yan ta’adda za su kwatanta kai hari a birnin Yamai mafarin abin da ya sa jami’an tsaro suka kaddamar da wani binciken ababen hawa.

Saurari cikakken rahoton Souley Moumouni Barma daga Yamai:

Your browser doesn’t support HTML5

'Yan bindiga Sun Kashe 'Yan sanda Biyu a Nijar - 2'48"