TUBALIN TSARO: Batun Sojojin Da 'Yan Bindiga Suka Kashe a Jihar Neja - Agusta 19, 2023

HAssan Maina Kaina

Shirin na wannan makon ya maida hankali ne kan aika aikar 'yan bindiga dadi da ke kara muni a jihar Neja da a baya bayan nan su ka yi sanadin rasa rayukan dimbin zaratan sojojin Najeriya,

A daidai lokacin da wasu dakarun su ka rasa rayukansu ne kuma wani jirgin saman sojojin saman kasar ya zo yankin da abin ya faru inda ya debi gawarwakin da ma sojojin da su ka sami rauni da niyyar jigilarsu zuwa kaduna.

A kan hanyarsa zuwa kadunan, jirgin ya yi hatsari inda aka sami rahotannin dake cin karo da juna dangane da musabbabin aukuwar hatsarin. To shin mene ne gaskiyar abin da ya faru?

Saurari cikakken shirin:

Your browser doesn’t support HTML5

TUBALIN TSARO