Tashin hankalin Ingila ya hana kwallon Nigeria da Ghana

  • Aliyu Mustapha

Tashin hankalin Ingila ya hana kwallon Nigeria da Ghana

Rigimar da ta kaure a sassa daban-daban na Ingila ta tilasta sa a soke muhimman wassanin kwallon kafa ciki harda na Nigeria da Ghana.

Tashin hankalin dake gudana a kasar Ingila ya janyo soke wasu muhimman wassanin kwallon kafa da aka shirya tsakanin kasashe daban-daban. Bayan mutuwar wani mutum da aka harbe yayinda yake zaune a cikin motarsa a London ne, aka bada sanarwar soke kwallon kafar da aka shirya yi tsakanin Ingila da Netherlands. Haka ita ma kwallon sada-zumunci da aka so yi tsakanin Nigeria da Ghana a nan Ingila din, an soke ta. Aliyu Mustaphan Sokoto ya zanta da shugaban hukumar kwallon kafar Nigeria Alhaji Aminu Maigari wanda yake a can Ingila gameda wannan kwallon: