‘Takararmu A Jam’iyyar Labour Ta Na Firgita ‘Yan Adawa – Dr Datti Baba-Ahmed 

Your browser doesn’t support HTML5

Mataimakin Peter Obi dake takarar shugaban kasa a Najeriya a jam’iyyar Labour, Dr Yusuf Datti Baba-Ahmed ya ce ‘yan siyasa na wasu jam’iyyu da magoya bayansu sun firgita da tasirin da jam’iyar Labour ke yi, wanda hakan ne ma ya sa wasu ke yamadidin cewa wai Peter Obi ya na shirin janye takararshi.