Sokoto Ta Janye Dalibai 39 Daga Jami’o'in Daular Larabawa

Gwamnatin Jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal, a lokacin ziyararsa a Sashen Hausa na Muryar Amurka

A wani mataki na tsuke bakin aljihu, gwamnatin Jihar Sokoto ta janye dalibanta 39 da ke karatu a jami’o'i daban daban a hadaddiyar Daular Larabawa.

Za kuma a maida su wasu jami’oi da ke Najeriya, kamar yadda gwamnatin jihar ta tabbatar.

Wannan mataki a cewa gwamnatin jihar ta Sokoto na nuni da irin fannonin da gwamnati za ta fi maida hankali a kai.

Akalla Naira miliyan 500 ake kashewa akan daliban su 39, kuma hukumomin jihar sun ce za su kara duba wasu fannonin da gwamnati ke kashe kudade masu dumbin yawa domin a rage ko kuma a soke.

Domin jin karin bayani saurari rahoton wakilinmu Murtal Faruk Sanyinna daga Sokoto:

Your browser doesn’t support HTML5

Sokoto Ta Janye Dalibai 39 Daga Jami’oin Daular Larabawa – 2’58”