Shugaba Macron Ya Ya Da Zangon Farko a Burkina Faso

Emmanuel Macron yayin da yake jawabi a ziyarar da ya kai Burkina Faso

Shugaban Faransa, Emmanuel Macron ya ya da zango na farko a Burkina Faso, yayin da yake rangadin wasu kasashen yammacin nahiyar Afirka, inda Faransa ta jibge dakarunta da dama domin yakar 'yan ta'adda.

Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya gana da takwaran aikinsa na Burkina Faso Roch Marc Christian Kabore a yau Talata cikin rangadin da zai kai shi kasashen Afirka uku.

Cikin abubuwan da aka gudanar a yau sun hada da jawabi ga daliban jami'a da kuma ganawa da 'yan Faransa da ke zama a Ouagadougou, babban birnin kasar.

Cikin muhimman batutuwa da aka fi maida hankali akai yayin wannan ziyara akwai batun tsaro, da samar da ayyukan yi, da muhalli, da kuma batun 'yan ci-rani.

Tattaunawa akan Matasan Afrika na daya daga cikin muhimman batutuwan da aka maida hankali akai har ila yau a lokacin taron koli na hadin gwiwa tsakanin jami'an Tarrayar Turai a Ivory Coast a gobe Laraba.

Daga bisani Shugaban na Faransa zai kai ziyara Ghana, ziyarar da babu shugaban Faransa da ya taba kaiwa.

A ziyarar shugaban na Faransa zai gana da matasa a Accra, babban birnin Ghana inda nan ne zai zamanto zangonsa na karshe.

Faransa na da dakurun sama da 7,000 a Afirkaa, hade da wadanda ke farautar ‘yan ta’adda a yankin Sahel, da hadin gwiwar sabuwar rundunar yaki da 'yan ta'adda da Macron ya taimaka wajen kafa ta.