NAKASA BA KASAWA BA: Martanin Masu Bukata Ta Musamman Kan Sakamakon Zaben Shugaban Najeriya, Maris 9, 2023

Souley Mummuni Barma

A ci gaba da bin diddigin yadda nakasassu suka gudanar da zaben da ya gabata a tarayyar Najeriya, shirin yau ya kai ziyara jihar Jigawa don jin abinda masu bukata ta musamman ke cewa bayan da hukumar INEC ta fitar da sakamakon zaben ranar 25 ga watan Fabrairu.

Kungiyoyin nakasassu a jihar ta Jigawa sun nuna gamsuwa da yadda aka ba su damar kada kuri’a daidai da tsarin da aka shimfida a can farko. Malam Ibrahim Issa wanda aka fi sani da Ibrahim Yaro garkuwan Hadejia, na daga cikin shugabannin guragun jihar Jigawa, ya yi bayani.

Saurari shirin cikin sauti.

Your browser doesn’t support HTML5

NAKASA BA KASAWA BA: Martanin Masu Bukata Ta Musamman Kan Sakamakon Zaben Shugaban Najeriya