Mutum 24 Suka Mutu Sakamakon Ruftawar Wani Babban Wurin Shara A Uganda

Kauyen Lusanja a wajen Kampala, Aug. 10, 2024.

Adadin wadanda suka mutu sakamakon ruftarwar wani tudun bola a babban birnin Uganda ya karu zuwa 24 a ranar Litinin din nan yayin da masu aikin ceto ke ci gaba da neman wadanda abin ya shafa a cewar hukumar birnin.

Akalla yara hudu na daga cikin wadanda rugujewar ta rutsa da su a Kiteezi ranar Juma’a, kamar yadda ‘yan sanda suka shaida wa manema labarai.

Uganda

Ana kyautata zaton ruwan sama ne ya janyo rugujewar wurin sharar. Ba a fayyace cikakkun bayanai game da abin da ya faru ba, amma hukumar birnin ta ce an samu "raguwar tsarin karfin wurin da dinbin shara."

Irene Nakasiita, mai magana da yawun kungiyar agaji ta Red Cross ta Uganda, ta ce babu wani sauran fatan ceto wasu mutane da ransu.

UGANDA

Ba a dai bayyana adadin mutanen da ba a ji duriyarsu ba. Wurin zubar da shara na Kiteezi wani babban juji ne a wani yanki mai fama da talauci wanda ke karbar daruruwan motocin dakon shara a kullum. Hukumar birnin ta yi niyyar soke shi tun bayan ayyana shi shekaru cikakku da suka gabata.

-AP