Mataimakin Shugaban Amurka ya Fayyace Matsayin Amurka Kan Tarzomar Iran

Mike Pence-Mataimaki Shugaban Amurka

Mataimakin shugaban kasar Amaurka Mike Pence ya lashi takobi cewa Amurka zata marawa masu zanga zangar kin jinin gwamnatin Iran baya kuma yace shugaba Donald Trump ya shirya yaba bada goyon baya ga masu zanga zangar ba da kalaman baki kadai ba.

A hirar da yayi da Greta Van Susteren, wata mai bada tarbacce ga shirye-shiryen gidan rediyon nan na VOA a ofishinsa a jiya Laraba, yace, da farko ya kamata a san cewa Iran itace kan gaba wurin bada tallafi a ayyukan ta’addanci a duniya.

Yace, baicin zalunci da take hakkokin al’ummanta, Iran tana kuma aika yan ta’adda zuwa wasu kasashe dake yankin sannan kiuma m tana ci gaba da zama kasar dake da tasiri mai yawa da kuma hatsari a wannan yankin.

Sai dai kuma Pence yaki bada da karin bayani a kan matakan da Amurka ka iya dauka kan wannan lamari na Iran, yana mai cewar, akwai matakan bada taimako na musamman da Amurka da sauran kasashen duniya zasu iya baiwa mutane Iran, idan suka ci gaba da dagewa wajen neman yancinsu.