Manyan Batutuwan Da Tinubu Ya Tabo A Jawabin Ranar Samun Yancin Kai Karo Na 64

Shugaba Tinubu

A yayin bikin cikar Najeriya shekaru 64 da samun ‘yancin kai, Shugaba Bola Tinubu ya yi jawabi ga al’ummar kasar inda ya yaba da irin gwagwarmayar da ‘yan Najeriya da dama suka fuskanta tare da bayyana irin kokarin da gwamnatinsa ke yi na shawo kan wadannan kalubale ta hanyar kawo sauyi mai dorewa.

Shugaba Tinubu ya fara ne da cewa yana sane da irin halin tsadar rayuwa da ake ciki, ya kuma tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa ana jin muryoyinsu, kuma gwamnatinsa ta dukufa wajen lalubo hanyoyin da za a bi domin rage musu radadin da suke ciki. Tinubu ya bukaci ‘yan Najeriya da su ci gaba da hakuri, yana mai cewa sauye-sauyen da ake ci gaba da samu sun fara bayyana.

Ci Gaban Najeriya Tun Bayan Samun 'Yancin Kai

Shugaban ya yi tsokaci kan tafiyar Najeriya tun bayan samun ‘yancin kai shekaru 64 da suka gabata. Ya bayyana irin tsayin daka da ci gaban kasar, inda ya jaddada yadda Najeriya ta jure rikice-rikice da dama da ka iya haddasa wargajewar wasu kasashe. Ya kuma ambato da rikicin siyasa da yakin basasar da Najeriya ta fuskanta jim kadan bayan samun ‘yancin kai, da kuma yadda al’ummar kasar tun daga lokacin suka koyi rungumar bambance-bambancen da ke tsakaninsu tare da kokarin samar da cikakken hadin kai.

Nasarar Tsaro A Yaki Da Ta'addanci

A bangaren tsaro kuwa, Shugaba Tinubu ya bayyana samun ci gaba a yaki da ta’addanci da ‘yan fashi da garkuwa da mutane. Ya bayyana cewa sama da kwamandojin Boko Haram 300 ne sojojin Najeriya suka kawar da su a yankin arewa maso gabas, arewa maso yamma da sauran yankunan da abin ya shafa. Dubban mutanen da rikici ya raba da muhallansu yanzu sun koma gidajensu, kuma an samu zaman lafiya a cikin al'ummomi da dama.

Tinubu ya yarda cewa duk da yake fadan bai kare ba, gwamnati ta kuduri aniyar kawar da duk wani nau'in ta'addanci. Maido da zaman lafiya da zai baiwa manoma damar komawa yankunansu, wanda hakan zai kara habaka noman abinci da kuma rage farashin kayan abinci.

Bayani Game Da Ibtila’o’i

Shugaban ya kuma yi jawabi kan ibtila’o’in da suka faru a baya-bayan nan, musamman ma ambaliyar ruwa da ta shafi sassan kasar. Ya kuma tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa gwamnatin tarayya na goyon bayansu a lokutan bukata kuma ana daukar matakan hana afkuwar bala’o’i a nan gaba. Wadannan sun hada da gudanar da gwaje-gwaje masu inganci akan madatsun ruwa a fadin kasar domin tabbatar da tsaro da ingancinsu.

Gyaran Tattalin Arziki da Zuba Jari

Shugaba Tinubu ya yi bayani kan sauye-sauyen tattalin arzikin da gwamnatinsa ke aiwatarwa domin daidaita kasar da kuma bunkasa ci gaba mai dorewa. Ya bayyana muhimmancin gyara kura-kuran kasafin kudi wanda ya haifar da koma bayan tattalin arziki a halin yanzu.

Shugaban ya tabbatar wa 'yan Najeriya cewa gwamnatin ta himmatu wajen samar da kasuwanci kyauta tare da kiyaye ka'idoji. Ya ba da misali da yadda ExxonMobil ta karkata a bangaren man fetur a matsayin misali na samun nasarar yin gyare-gyare a harkar mai da iskar gas, wanda ake sa ran zai kara yawan hakowa da kuma tasiri ga tattalin arziki.

Gudanar da Kudi da Rage Bashi

Tinubu ya kuma bayar da rahoton ci gaban da aka samu wajen kula da asusun ajiyar Najeriya da basussukan kasashen waje. Gwamnatin ta gaji dala biliyan 33 a asusun kasashen waje kuma tun daga nan ta mayar da dala biliyan 7 da aka samu ta barauniyar hanya yayin da ta rage yawan bashin kasar daga kashi 97% zuwa 68%. Duk da wannan ƙoƙarce-ƙoƙarce, asusun ajiyar waje ya tsaya akan dala biliyan 37.

Tinubu ya kuma jaddada cewa wadannan matakan kasafin kudi na da matukar muhimmanci wajen tabbatar da dorewar tattalin arziki da samar da karin ayyukan yi.

Haɓaka Noma

A wani bangare na kokarin magance tsadar kayan abinci, shugaban ya yi kira ga jihohi da su sanya hannun jari a harkar noma, inda ya bayyana shirin noman da jihohi kamar Jigawa, Neja, da Nasarawa suka runguma gadan-gadan.

Gwamnatin tarayya na tallafa wa wadannan yunƙuri ta hanyar samar da taki, tarakta, da sauran kayan aikin gona. Ana kuma ci gaba da aikin harhada injinan gonaki, inda ake sa ran kammala aikin cikin watanni shida, inji shugaban na Najeriya

Ƙaddamarwar Makamashi da Harkokin Sufuri

Shugaba Tinubu ya tabo batun wutar lantarki a Najeriya, musamman fadada iskar gas samfurin (CNG) a madadin man sufuri.

Yace “Gwamnati na haɗin gwiwa da kamfanoni masu zaman kansu don sauƙaƙe wannan sauyin kuma ta himmatu don taimakawa jihohi su sami motocin CNG don jigilar jama'a mai rahusa.”

Ƙarfafa Matasa da Samar da Aiki

Ganin cewa sama da kashi 60% na al’ummar Najeriya matasa ne, shugaban ya bayyana shirin taron matasa na kasa. Wannan taron zai tattaro matasa daga sassa daban-daban na kasar don tattaunawa kan kalubale kamar ilimi, aikin yi, da tabbatar da zaman lafiya. Za’a yi taron ne da nufin karfafawa matasa gwiwa su taka rawar gani wajen gina kasa.

Har ila yau, gwamnatin na aiwatar da shirye-shirye daban-daban da suka shafi matasa, ciki har da wani shiri na bunkasa hazaka da nufin horar da ‘yan Najeriya miliyan 3 fasahar zamani. Bugu da kari, Asusun ba da lamuni na Ilimi na Najeriya zai ba da lamuni mai araha ga daliban da ke neman ilimi mai zurfi.

Kiran Hadin Kai da Fatan Alkhairi ga Makomar Najeriya

Shugaba Tinubu ya kammala jawabinsa da yin kira ga hadin kai, inda ya bukaci ‘yan Najeriya da su ci gaba da hada kai domin gina kasa mai karfi da wadata. Ya jaddada cewa duk da kalubalen da ake fuskanta, kwanaki masu kyau na nan gaba, kuma tsayin daka na al'ummar Najeriya zai sa al'ummar kasar suyi nasara a cikin gwagwarmayar da suke ciki.

Ya kuma karfafa gwiwar kowane dan kasa da ya yi imani da yuwuwar kasar, yana mai cewa , Nijeriya za ta samar da kyakkyawar makoma nan da wasu lokuta kalilan masu zuwa.

Jawabin shugaban wanda ya tabo nasarorin da Najeriya ta samu, da kalubalen da ake fuskanta, da kuma damar da za ta samu a nan gaba. Sakon nasa na bege da rokon ‘yan Najeriya da su cigaba da hakuri, nasara na nan zuwa nan da lokaci kadan.

~Yusuf Aminu Yusuf~