Mahaukaciyar Guguwa Ta Ratsa Ta Jihar Mississipi

Hukumar kula da yanayi ta kasar Amurka ta ce wata mahaukaciyar guguwa ta far ma jihar Mississippi da ke yankin kudu maso gabashin Amurka da yammacin jiya Talata, guguwar ta yi sanadiyyar lalata wani shagon saida kayayyaki da ma wasu gidaje dake kan iyaka da jihar Alabama, yayin da iskar ta ketara zuwa kudancin kasar.

Rahotannin farko da aka samu daga cibiyar kula da yanayin kasar ya nuna cewa, da yammacin jiya Talata ne guguwar ta soma a garin Tishomingo dake arewa masu gabashin Jahar Mississippi.

Jami’an ‘yan sandan Tishomingo sun sanar ta wata kafar yada labaran yankin cewa, wasu sun dan yi rauni sai dai kuma, wani kantin rahusa da ake kira DOLLAR GENERAL ya tafka babbar asara.

An aika da sakon hasashen yanayin zuwa sauran yankin kudancin kasar da suka hada da wasu sassan jihar Tennessee da Georgia, an kuma yi gargadin cewa za a iya ci gaba da fuskantar barazanar yanayi a yau Laraba.