Jaruma Rashida Mai Sa’a Ta Yi Aure

Rashida Adamu Abdullahi Mai Sa'a da angonta (Hoto: Instagram/Sadamcy/Ali Nuhu)

Tuni kuma abokan sana’arta da masoyanta suka yi ta taya ta murnar wannan aure tare da yi mata addu'ar samun zaman lafiya.

Fitacciyar jarumar masana’antar Kannywood, Rashida Adamu Abdullahi (Mai Sa’a) ta shiga daga ciki.

An daura auren ne a ranar Asabar a birnin Kano da ke arewa maso yammacin Najeriya kamar yadda rahotanni suka nuna.

Tun a ranar Juma’a aka fara shagulgulan wannan biki wanda ya samu halartar manyan jarumai mata da maza da sauran masu ruwa da tsaki a harkar shirya fina-finai.

Tuni kuma abokan sana’arta da masoyanta suka yi ta taya ta murnar wannan aure tare da yi mata addu'ar samun zaman lafiya.

“Allah ya bada zaman lafiya kanwata @rashidamaisaa" In ji jarumi Ali Nuhu.

"Allah ya ba ku zaman lafiya." In ji Zainab Abdullahi 910.

"Allah ya sanya alheri." Nura Nayababa ya ce a shafin Facebook.