Gwamnatin Syria da Mayakan 'Yan Tawye Sun Cimma Yarjejeniya

Masu ficewa daga birnin Aleppo da yaki ya daidaita

Mayakan yan tawaye da gwamnatin Syria sun cimma yarjejeniyar tsagaita wuta don bada daman kwashe fararen hula da mayakan yan adawa daga gabashin birnin Aleppo, a yayid da Rasha take cewar gwamnatin Bashar al-Assad ta kawo karshen hare harenta a kan birnin.

Kakakin kungiyar yan tawayen ta Nour el-Din el-Zink, Yasser al-Youssef shine ya bayyana yarjejeniyar a jiya Talata da kasashen Rahsa da Turkiya suka shiga Tsakani wadda zata fara aiki nan da wasu sa’o’i.

Jakadan Rasha a Majalisar Dinkin Duniya ko MDD Vitaly Churkin ya tabbatarwa manema labarai da wannan yarjejeniyar tun kafin zaman gaggawa na kwamitin sulhun MDD a kan birnin Aleppo wanda Faransa da Birtaniya suka kira.

Jakadan yace sun samu labarin tsagaita ayyukan soji a gabashin birnin Aleppo, kuma yankin ya sake komawa karkashin rikon gwamnati, don haka za'a iya gudanar da manyan ayyukan agaji a yankin.

Churkin yace akasarin mayakan suna barin gabashin birnin Aleppo suna komawa garin Idlib.

Sai dai kuma manzon MDD a Syria Staffan de Mistura ya bayyana damuwarsa cewar garin Idlib zai iya zama wurinda munanan hare haren zasu koma.