Gwamnatin Filato Ta Shirya Maida 'Yan Gudun Hijira Gidajensu

'Yan Gudun Hijira A Jihar Filato

Gwamnatin jahar Filato ta ce ta kammala dukkan shirye-shirye don maida dukkan wadanda suka kaurace wa mahallansu, su ke kuma gudun hijira a wasu wurare, zuwa yankunansu na asali.

Komishinan ayyuka na musamman a jahar Filato, Irmiya Werr ya ce gwamnan jahar Simon Lalong, ya bada umurnin maida ‘yan gudun hijirar.

'Yan Gudun Hijira A Jihar Filato

Shugaban karamar hukumar Barikin Ladi, Barista Ezekiel Mandyau, ya ce sun yi zaman tattaunawa da masu ruwa da tsaki, sun kuma amince kowa ya koma gidansa.

'Yan Gudun Hijira A Jihar Filato

Shi kuma shugaban karamar hukumar Riyom, Mafeng Gwalson, ya bada tabbacin cewa gwamnati ta sanya matakan tsaro a yankunan domin ganin kowa ya zauna lafiya.

Wasu ‘yan gudun hjirar, sun yi na’am da matakan mayar da su garuruwansu.

A saurari rahoto cikin sauti.

Your browser doesn’t support HTML5

Gwamnatin Filato Ta Shirya Maida 'Yan Gudun Hijira Gidajensu