Firai Ministan Kasar Turkiyya Ya Kai Ziyara Kasar China

Primiyan kasar China Wen Jiabao, ta hannu hagu, tare da Firai Ministan Turkiyya Recep Tayyip Erdogan ta hannu dama, bayan ya isa birnin Beijing

Wannan ce ziyarar da wani Firai Ministan Turkiyya ya kai China cikin shekaru 27

Firai Ministan kasar Turkiyya Recep Tayyip Erdogan ya na kasar China, inda zai gana da manyan jami’an gwamnatin kasar domin su kulla huldar kut da kut a fannin cinikayya da siyasa.

A ziyarar aikin da wani firai ministan kasar Turkiyya ya kai China cikin shekaru 27, Mr.Erdogan ya samu tarbon karramawa da shimfidar jan darduma da kade-kaden taken kasashen biyu, da kuma jerin jami’an tsaron ban girma a Beijing. A yau Litinin zai gana da shugaba Hu Jintao da Pirimiya Wen Jiabao da kuma mataimakin shugaban kasa Xi Jinping.

Ministan makamashin kasar Turkiyya, Taner Yildiz ya ce a yayin ziyarar da Mr.Erdogan ya ke yi a kasar China, gwamnatin kasar Turkiyya za ta yanke shawara ko za a gayyaci Chinar ta ginawa Turkiyya masana’antar makamashin nukiliya a gabar tekun Bahar Aswad. Bangarorin biyu za su daddale batun gina masana’antar a yayin wannan ziyara.

Kafin Mr.Erdogan ya isa birnin Beijing tare da wata tawagar ‘yan kasuwa 300, sai da ya fara yada zango a jiya Lahadi a yankin Xinjiang a can gabashin kasar China mai nisa. Yankin na Xinjiang mai fama da tashin hankali, mazauni ne ga ‘yan kabilar Uighur (wee-goor) ‘yan tsiraru, wadanda ke da dangantakar kabila da Turkawa. Turkiyya na so ta kafa masana’antu a yankin na Xinjiang. Mr.Erdogan zai kammala ziyarar shi da Shanghai.