Faransawa Na Ci Gaba Da Jimamin Wadanda Suka Mutu Ko Suka Ji rauni

Ma'aiukatan agaji su na duba mutanen da aka kashe ko aka ji musu rauni a kofar wani gidan abinci a Paris.

'Yan sanda su na yin sintiri a gundumar nan ta Place de la Republique dake birnin Paris asabar, kwana guda a bayan wasu munanan hare-haren da suka kashe mutane fiye da 100.

Sojojin Faransa su na yin sintiri a kusa da hasumiyar nan ta Eiffel Tower, kwana guda a bayan munanan hare-hare a birnin Paris.

Wasu daga cikin wadanda suka kubuta da rayukansu a dakin wasa na Bataclan dake Paris a daren Jumma'a 13 Nuwamba, 2015.

Shugaba Francois Hollande yana jawabi ga al'ummar Faransa a bayan hare-haren ta'addancin da kungiyar ISI ta ce ita ce ta kai a daren jumma'a 13 Nuwamba, 2015. Shugaban ya ce duk mai hannu a wadannan hare-haren zai gwammace kida da rawa.

Wani mutumi ya rike kai a lokacin da yake ajiye furanni na jimami a kofar wani gidan abinci mai suna Carillon cafe, a Paris, Nov.14, 2015.

Taswirar wuraren da aka kai ma hare-hare a birnin Paris.

Wasu 'yan jarida su na aiki a kofar wani gidan abinci inda ake iya ganin yadda harsashi ya huda gilashin kofar a Paris.

Mutane su na wucewa ta jikin farfajiyar da aka killace ta gidan wasa na Bataclan, kwana guda a bayan mummunan harin da ya kashe mutane da yawa cikin dakin wasan dake Paris.

'Yan sandan Faransa su na binciken motoci a bakin iyakar kasar da Italiya, kusa da La Turbie, asabar 14 Nuwamba, 2015.

A bayan hare-haren da suka kashe mutane akalla 127, wadanda kungiyar ISI ta ce ita ce ta kai, Faransawa su na ci gaba da jimami yayin da shugabanninsu ke lasar takobin cewa wadanda suka kai zasu ga tashin hankali.