Dangote Ya Ba 'Yan Gudun Hijira A Nijar Gudunmawa Ta Kimanin Dala Dubu 500,000

Aliko Dangote

Shahararran dan kasuwan nan na kasar Najeriya, Aliko Dangote, ya tallafawa 'yan gudun hijiran Najeriya dake zaune a jihar Maradi ta jamhuriyar Nijar, wadanda 'yan bindiga, da masu garkuwa, ko kuma mutane suka koro.

Treloli goma sha shidda, cike da kayan abinci, da na masarufi wanda a
cewar Gwamnan jihar Maradi Zakari Umaru, ya tashi kimanin million dari
ukku na sefa. Ya kara da cewa, da ma akwai irin su PAM, da HCR, da Gwamnan Sokkoto, da NEMA ta Najeriya dake taimaka musu, kuma an yi musu rijiyoyi sannan ana basu magunguna.

Yanzu haka dai babbar damuwar su, har ma da 'yan gudun hijiran, ingantaccen tsaro ya dawo domin su koma garuruwan su. Wannan shine dalilin da yasa Gwamna Zakari, ya rubuta wa hukumomin yankunan Najeriya wasiku domin su zauna, su samo mafita.

Su ma bayan godiya 'yan gudun hijiran, sun bayanna wa wakiliyar Muryar Amurka Tamar Abari, fatan su na komawa cikin 'yan uwansu, da garuruwansu na ainahi.

A saurari cikakken rahoton daga wakiliyar Muryar Amurka Tamar Abari.

Your browser doesn’t support HTML5

Dangote Ya Kai Gudunmawa Kimani $500 Mliyan Wa 'Yan Gudun Hijira