Dan Kunar Bakin Wake Yayi Shigar 'Yan Sanda Ya Kashe Mutane A Mogadishu

Wani Harin Ta'addanci

Akalla mutane 17 ne suka rasa rayukansu, sannan wasu 15 suka jikkata bayan da wani dan kunar bakin wake ya tarwatsa kansa a babban ginin horar da ‘yan sandan kasar da ke babban birnin Mogadishu a yau Alhamis.

Akalla mutane 17 ne suka rasa rayukansu, sannan wasu 15 suka jikkata bayan da wani dan kunar bakin wake ya tarwatsa kansa a babban ginin horar da ‘yan sandan kasar da ke babban birnin Mogadishu a yau Alhamis.

Wannan hari ya faru ne yayin da ‘yan sanda suke bitar fareti a cibiyar horar da ‘yan sanda ta Janar Kahiye Police Academy. Jami’ai sun ce maharin yayi shigar burtu ne, inda ya saka kaya irin na ‘yan sanda. Sai dai hukumomi ba su ba da takamaiman adadin wadanda suka mutu ba, kuma tuni Kungiyar Al Shebab suka dauki alhakin kai wannan harin.

Wani rahoton Majalisar Dinkin Duniya da aka hada bayan binciken da aka gudanar cikin watanni 20 da suka gabata, ya nuna cewa baya ga jami'an tsaro, hare-haren kungiyar Al Shebab na ci gaba da shafar fararen hula.