Da Alama Shugaban Amurka Donald Trump Zai Cire Kasar daga Yarjejeniyar Nukiliyar Iran

Shugaban Amurka Donald Trump yayinda yake nuna kin amincewarsa da yarjejeniya

Ana kyautata zaton mako mai zuwa ne shugaban Amurka Donald Trump zai janye kasarsa daga yarjejeniyar nukiliyar Iran wadda aka cimma a shekarar 2015 lokacin gwamnatin Barack Obama

Wasu manyan jami’an gwamnatin Amurka sun ce, akwai yiwuwar, shugaba Donald Trump, ya cire hannun kasar a yarjeniyar nukiliya da aka kulla da Iran, sannan ya nemi majalisar dokokin kasar ta sabunta wasu takunkumi a kan kasar.

A makon da ke tafe ake sa ran shugaba Trump zai bayyana shirinsa na daukan wannan mataki, a wani jawabi da zai yi, domin a cewar jami’an gwamnatin kasar, matsayar da aka cimma da Iran, ba ta kare wani muradin Amurka.

Sai dai wannan mataki ba wai zai soke matsayar da aka cimma ba ne a shekarar 2015, amma zai sa a maida zancen gaban majalisar dokokin Amurka ne, inda majalisar ke da kwanaki 60 ta yanke shawarar ko a mayar da takunkuman da aka dagewa kasar ta Iran bayan da aka kulla yarjeniyar, ko kuma aksain haka.

Cire hannun Amurka a wannan matsaya da aka cimma, zai iya bude kofar sake yin dubi kan shirin, amma kuma shugaban Iran Hassan Rouhani ya ce wannan ba zabi ba ne.

A duk kwanaki 90, sai Shugaba Trump ya bayyana ko Iran tana bin matakan da aka gindaya mata a karkashin shirin.

Sai dai a wata ganawa da ya yi da manyan hafsoshin sojin kasar a jiya Alhamis, Trump ya natata matsayarsa cewa Iran ba ta bin ka’idojin da aka gindaya mata.