Buhari Na Dab Da Rattabawa Kasafin Kudin 2018 Hannu

Shugaba Muhammadu Buhari

A wata sanarwar da mai ba Shugaba Buhari shawara akan harkokin yada labarai, Femi Adesina ya fitar, ya bayyana cewa Shugaba Muhammadu Buhari zai rattaba hannu a kasafin kudin shekarar 2018 nan ba da jimawa ba.

Shugaban kwamitin kasafin kudi na majalisar dattawan Najeriya, Sanata Danjuma Goje ya fadi dalilan jinkirin da aka samu, inda ya ce ministoci da yawa ba su je suka kare ma'aikatansu ba har sai da shugaban kasa ya tsawata musu.


Daga wannan kasafin dai ma'aikata a Najeriya na sa ran karin albashi zuwa watan Disamba, duk da cewa hakan bai zama lallai ba.Shugaban kungiyar kwadago ta NLC ya ce tashin farashin muhimman lamura na rayuwa na haddasa radadi ga ma'aikata.
.

Your browser doesn’t support HTML5

Buhari Na Gab Da Sanya Wa Kasafin 2018 Hannu- 2' 38"