AREWA A YAU: Dalilan Da Su Ka Kawo Tarnaki Ga Tattalin Arziki A Arewa - Nuwamba 15, 2023

Nasiru Adamu El-Hiyaka Lokacin Kan Hanyar Kaduna Zuwa Abuja

Sabon shirin Arewa A Yau zai duba dalilan da su ka kawo tarnaki ga tattalin arziki a arewa, musamman tun daga hanyoyin samun abun dogaro da kai daga gidaje, cikin anguwanni da kuma garuruwa.

Kwararre a kimiyyar kididdiga, Farfesa Sadik Umar Abubakar, ya yi bayani filla-filla.

Daga nan za mu kawo karshen bayanin Dr. Kole Shettima kan muhimmancin gidauniyar ilimi don tallafawa dimbin yara da ke arewa da ba sa samun sukunin zuwa makaranta.

Farfesa Sadik Umar ya yi ninkaya a cikin tarihi inda ya duba yanda a ka fara har lamura su ka zama masu wuya.

Saurari rahoton:

Your browser doesn’t support HTML5

AREWA A YAU