AREWA A YAU: Batun Hare-Hare Kan 'Yan Kasuwar Arewa A Wasu Yankunan Kudu, Musamman Fataken Shanu - Oktoba 25, 2023

Nasiru Adamu El-Hiyaka Lokacin Kan Hanyar Kaduna Zuwa Abuja

Sabon shirin AREWA A YAU ya duba karfafa bukatar kungiyoyin arewa 115 su kafa wata kasuwa kan iyakar arewa da kudu inda 'yan kasuwa za su rika kai kaya don cinikayya tsakanin sassan biyu na Najeriya ba tare da samun asara ba. Wannan tamkar kandagarki ne na irin yadda a baya ake samun hare-hare kan fatake daga arewa da kan kai hajojinsu kudu.

Daga nan mun sake duba yadda rashin makarantu masu ba da shaidar karatu mai daraja ta biyu a arewa ya kawo kalubalen koyarwa a arewa.

Saurari shirin cikin sauti:

Your browser doesn’t support HTML5

AREWA A YAU