An Shirya Taron Sulhu Tsakanin Matasa a Jihar Flato

Jos

Rundunar ta musamman dake aikin tsaro da zaman lafiya a jihar Flato ta shirya taro tsakanin matasa a kudancin jihar Flato.
Da yake jawabi a bikin bude taron, kwamandan rundunar tabbatar da zamaan lafiya a jihar, Manjo janar Henry Ayola, ya shawarci matasan da su gafartawa juna.

Kamar yadda wakiliyarmu a yankin Zainab Babaji ta aiko, yankin kudancin jihar da ya kunshi kananan hukumomi shida sun fuskanci matsaloli da suka hada da kisa, da sace sacen dabbobi, da kone konen gidaje.

Your browser doesn’t support HTML5

Taron sulhu a Jihar Flato - 9:59