An Kafa Tarihin Nada Dan Kabilar Igbo Limami A Masallacin Kasa Na Abuja

  • VOA Hausa

Masallacin kasa na Abuja (Foto: REUTERS/Afolabi Sotunde)

A wani babban al’amarin da ya shafi al’ummar Musulmin Najeriya, an nada Farfesa Ilyasu Usman, dan kabilar Igbo na farko, a matsayin limamin masallacin kasa na Abuja.

Yau ta kasance muhimmiyar ranar da sabon limamin ya gabatar da hudubarsa ta sallar Juma’a, matakin da ya zamo abin alfahari ga Musulmin Najeriya baki-daya.

Farfesa Ilyasu Usman

Hukumar gudanarwar babban masallacin kasa na Abuja ta gano tarin gudunmowar da Farfesa Usman ya baiwa ilimin addinin Musulunci, kuma ana ganin nadin nasa a matsayin wata nasara wajen kara hadin kan al’ummar Musulmi.

Kungiyar Musulmi ‘yan asalin yankin kudu maso gabashin Najeriya (SEMON) ta yi maraba da wannan shawara, inda ta yabawa nadin nasa a matsayin manuniya ga irin gudunmowar daya bayar wajen hidimtawa addinin Musulunci da harkokin jagorancinsa.