An Kafa Hukumar Kare Iyakokin Kasashen Turai

Wasu Yan Gudun Hijira

Kungiyar Tarayyar Turai ta bada sanarwar kafa wata sabuwar Hukumar Iyakoki da zata rinka sa dogarawa suna zagaya kan iyakokin kasashen Turai don hana shigowar ‘yan gudun hijira daga kasashen Afrika da na Larabawa.

Wannan sabuwar hukumar zata yi aiki ne da ma’aikatun kan iyakokin da daman ake da su a cikin kasashen 28 dake cikin K-T-T din, inda zasu hada kai su rinka bankado duk wata barazana ga harakokin tsaron kasashen.

Haka kuma sabuwar hukumar, wacce zata fara aiki a watan Maris na 2017, zata taimaka wajen ganin an sawwaka musayar bayanai a tsakanin ma’aikatin tsaro da na leken assirai na kasashen da abin ya shafa, a cewar Fabrice Leggeri, Darektan Hukumar Kan Iyakokin na Turai.

Rahottani sunce kafa Hukumar yana faruwa ne a sanadin dimbin yawan ‘yan gudun hijiran da suka rinka kwarara a cikin kasashen Turan a ‘yan shekarun nan, wanda akace ba’a ga mai yawansu ba tun karshen Yakin Duniya na Biyu.

A shekarar da ta gabata kadai, kasashen Turai sun karbi bakuncin bakin haure sun kai milyan 1 da dubu 500.