Abin Da Masu Sharhi Ke Cewa Kan Makomar Mayakan Boko Haram Da Ke Mika Wuya A Najeriya

Your browser doesn’t support HTML5

A Najeriya, har yanzu ana ci gaba da tsokaci dangane da yadda mayakan Boko Haram ke mika wuya yayin da dakarun kasar ke ikirarin samun galaba akan mayakan.
Rundunar sojin Najeriya ta ce kawo yanzu kimanin ‘yan Boko Haram da iyalansu dubu takwas ne suka mika wuya ga hukumomi a baya-bayan nan. Mika wuya da mayakan ke ci gaba da yi dai ya haifar da muhawara a Najeriyar a game da makomarsu. Farfesa Khalifa Ali Dikwa, mai fashin baki ne akan al’amuran yau da kullum.