Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Zanga-Zanga: Amurka, Birtaniya Da Canada Sun Bukaci ‘Yan Kasarsu Su Yi Hattara


ABUJA: Tambarin Ofishin Jakadancin Amurka a Najeriya
ABUJA: Tambarin Ofishin Jakadancin Amurka a Najeriya

Amurka da Birtaniya da kuma Canada sun fitar da sanarwar gargadi ga ‘yan kasashensu mazauna a Najeriya, kan su zauna cikin shiri kan yiwuwar barkewar rikici yayin zanga-zangar da aka shirya za a yi a kasar.

Kiraye-kiryen na zuwa ne a daidai lokacin da ake shirin gudanar da zanga-zangar adawa da yunwa da wahalhalu a fadin kasar daga ranar 1 ga Agusta, 2024.

A cikin shawarwari ga matafiya daban-daban, kasashen uku sun gargadi 'yan kasarsu da su guji wuraren da za a iya samun arangama tsakanin hukumomin tsaro da masu zanga-zangar.

A nata shawarar, Ofishin Jakadancin Amurka a Abuja ya bukaci Amurkawa da su guji gudanar da tarukan, inda ta shawarce su da su nisanta kansu daga cunkoson jama’a da zanga-zangar da kuma ci gaba da samun labarai ta kafafen yada labarai na ciki gida. https://tinyurl.com/28943fy3

Sanarwar ta kara da cewa, akwai yiwuwar toshe hanya, wuraren binciken ababen hawa, cunkoson ababen hawa, da kuma yin taho-mu-gama, inda ta bayyana cewa, “a cewar rahotannin kafafen yada labarai, ana iya samun zanga-zanga a fadin kasar a Najeriya tsakanin 29 ga Yuli zuwa 5 ga watan Agusta, 2024.

Bisa la’akari da abubuwan da suka faru a baya, zanga-zangar na iya haifar da shingaye, wuraren binciken ababen hawa, cunkoson ababen hawa, da kuma gwabzawa fada”.

Hakazalika, babbar hukumar Birtaniya ita ma ta yi gargadin cewa za a iya gudanar da zanga-zanga tsakanin ranakun 29 ga watan Yuli zuwa 10 ga watan Agusta a manyan biranen Abuja da Legas https://tinyurl.com/25j8878s.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG