Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Zaben 2023: INEC Ta Kammala Shiri Don Zaben Gwamnoni Da Na ‘Yan Majalisar Jiha


Zaben gwamnoni 2023
Zaben gwamnoni 2023

Hukumar zaben Najeriya ta INEC ta ba da tabbacin kammala dukkan shirye-shirye don gudanar da zaben gwamnoni da na ‘yan majalisar jiha a jihohi 28 na kasar ranar Asabar 18 ga watan Maris.

Hukumar INEC dai ta dage lokacin zaben na gwamnoni da mako guda zuwa yau Asabar. Za a gudanar da zabukan ne a jihohi 28, yayin da sauran jihohi 8 na kasar lokacin zabensu dabam da sauran, sakamakon hukuncin kotu a baya da ya sauya lokutan zabensu.

Akalla manyan jam’iyyun APC da PDP na da ‘yan takara a dukkan jihohi inda wasu jam’iyyu da suka hada da NNPP, Labour, SDP, YPP da sauransu suka tsayar da nasu ‘yan takarar da dama.

Zaben 2023
Zaben 2023

Tun a zanga-zangar da ‘yan adawa suka yi zuwa hukumar INEC kan cewa BVAS ba ta yi aiki ba a zaben shugaban kasa, INEC a ta bakin jami’a a sashen yada labaran hukumar Zainab Aminu, ta nanata batun shirin aiki da BVAS a zaben na yau.

Da karfe 2.30 na ranar Asabar agogon Najeriya za a rufe rumfunan zabe, amma duk wanda ke kan layi zai samu damar kada kuri’a ko karfe nawa hakan zai dauka.

Saurari rahoton Nasiru Adamu Elhikaya:

please wait

No media source currently available

0:00 0:01:00 0:00
XS
SM
MD
LG