Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Yau juma'a aka shirya za'a rantsar da sabon shugaban Ivory Coast


Shugaban Ivory Coast, Alassane Ouattara a birnin Abidja.
Shugaban Ivory Coast, Alassane Ouattara a birnin Abidja.

Hukumar lura da kundin tsarin kasar Ivory Coast tace a yau juma'a za'a rantsar da Alassane Ouattara a zaman shugaban kasa. A jiya kotun kolin kasar ta ayyana Ouattara a zaman wanda ya lashe zaben shugaban kasar da aka yi a bara.

Hukumar dake lura da kundin tsarn mulkin kasar Ivory Coast tace a yau juma'a za'a rantsar da Alassane Ouattara a zaman shugaban kasar. A jiya Alhamis kotun kolin kasar ta yanke hukuncin ayyana cewa Mr Ouattara ne ya lashe zaben shugaban kasar da aka yi a bara da kashi hamsin da hudu daga cikin dari na kuri'un da aka kada. Matakin daya kauda hukuncin da wata kotu ta yanke cewa tsohon shugaba Lauren Gbagbo shine ya lashe zaben. Mr Gbagbo yayi amfani da hukuncin farko ya makalewa jan ragamar mulkin kasar. Kiyawar da yayi na sauka daga kan mulki ya hadasa tarzomar watani hudu ta fafitukar iko data zama sanadin mutuwar daruruwan mutane kuma imamin mutum miliyan guda suka rasa matsuguninsu. A watan jiya Mr Ouattara ya dare kan ragamar mulki bayan da magoya bayansa suka kama bijirerren Mr Gbagbo a gidansa dake birnin Abidjan tare da taimakon sojojin Majalisar Dinkin Duniya dana kasar Faransa. A wani labarin kuma a jiya Alhamis Amirka tace zata baiwa kasar Ivory Coast karin taimakon dala miliyan takwas da rabi domin taimakon wadanda suka arce daga gidajensu a sakamakon rikicin siyasar da aka yi a kasar. Jami'an Amirka sunce za'a yi amfani da udin wajen samar da ruwa da magunguna da kuma wasu kayayyakin masarufi.

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG