Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Wni Harin Isra'ila a Arewacin Gaza Ya Hallaka Akalla Mutum 22


A Palestinian inspects the damage after an overnight Israeli airstrike in Beit Lahia the northern Gaza Strip on October 27, 2024 amid the ongoing war in the Palestinian territory between Israel and Hamas.
A Palestinian inspects the damage after an overnight Israeli airstrike in Beit Lahia the northern Gaza Strip on October 27, 2024 amid the ongoing war in the Palestinian territory between Israel and Hamas.

Likitocin Isra’ila sun ce wata babbar mota tayi karo da wata motar safa a daura da Tel Aviv, wanda yayi sanadiyyar jikkata mutum 35.

Jami’an Falasdinu sun ce wani farmakin Isra’ila a arewacin Gaza ya kashe akalla mutane 22 da galibin su mata da yara ne. Hare haren da Isra’ila ta kai yankin da aka daidaita sannan mutane sukakaurace mishi ya shiga mako na 3 yau Lahadi yayin da kungiyoyin bada agajin jinkai suka bayyana bala'i a game da batun agajin jinkai.

A wani bangaren kuma, likitocin Isra’ila sun ce wata babbar mota tayi karo da wata motar safa a daura da Tel Aviv, wanda yayi sanadiyyar jikkata mutum 35.

Sannan, a gefe guda kuma, shugaban Adninin Iran ya ce “Kada a kururuta ko a sassauta hare haren da Isra’ila ta kai Iran cikin karshen makon nan, yayin da bai yi kira da mai da a da martini ba, lamarin da ake ganin yana nufin cewa Iran tana auna matakin da zata dauka nan gaba cikin tsanaki.

A ranar Asabar ne, jiragen yakin Isra’ila sun kai hari cikin Iran a matsayin harin gayya na harin makaman mizile din da Iran ta kai mata a farkon wannan watan na Oktoba.

Dandalin Mu Tattauna

TASKAR VOA: Yadda Tsofaffi Ke Fama Da Lalular Yanar Ido A Nijar
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:26 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG