Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Nana Shettima Tayi Taron Gaggawa Akan Cibok


Wasu cikin iyayen daliban da aka sace a Cibok dake Jihar Borno.
Wasu cikin iyayen daliban da aka sace a Cibok dake Jihar Borno.

Kusan makonni uku ke nan da wasu 'yan bindiga suka sace dalibai fiye da dari biyu a makarantar 'yan mata dake garin Chibok lamarin da ya tayar da hankanli al'ummar Najeriya gaba daya.

Da gwamnatin jihar Borno da iyayen daliban da aka sace babu wanda yake cikin kwanciyar hankali lamarin da ya sa gwanatin jihar ta rufe makarantun jihar.

Uwargidan gwamnan jihar Bornon Hajiya Nana Kashim Shettima ta kira wani taron gaggawa a fadar gwamnatin jihar domin tattauna hanyoyin da za'a bi a kubuto daliban. Kawo yanzu babu wanda ya san halin da suke ciki. Mata da dama da suka tashi su yi jawabi akan hanyoyin da za'a bi sun yi hawaye.

Yayin da take jawabi da matan tace ta kira taron ne domin sace 'ya'yansu da wasu 'yan bindiga suka yi. Tace matsalar ba abun damuwa bane kawai abun bakin ciki ne. Lokacin da take jawabi matar gwamnan sai ta bige da kuka. Ta shaidawa matan su manta da batun kabilanci ko banbancin siyasa su fuskanci matsalar dake gabansu. Tace ta san zasu iya kuma Allah Yana tare da su.

Bayan an kammala taron Muryar Amurka ya zanta da shugabannin wasu kungiyoyi mata da suka halarci taron.Wata Esther tace shiri da iko suna wurin Allah. Tace magana ce dake bukatar addu'a. A cigaba da addu'a tare da azumi ba dare ba rana. Ita ma Hajiya Halima Abubakar ta kira 'yan bindigan su ji tsoron Allah su saki 'yan matan cikin koshin lafiya. Ta kira a yi addu'a dakuma rokon Allah akan zaman lafiya. Duk shugabannin kungiyoyin mata da suka yi magana sun roki 'yan bindigan su ji tsoron Allah su sako daliban.

Ga karin rahoto.
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:48 0:00
Shiga Kai Tsaye
Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG